50. Qaf - Alqur'ani
- 1. ¡̃. Inã rantsuwa da Alƙur`ãni Mai girma.
- 2. Ã`a, sun yi mãmãki, cewa mai gargaɗi, daga gare su, yã zo musu, sai kãfirai suka ce: "Wannan wani abu ne mai ban mãmãki."
- 3. "Shin idan muka mutu kuma muka kasance turɓãya (zã a kõmo da mu)? Waccan kõmowa ce mai nĩsa."
- 4. Lalle ne Mun san abin da ƙasã ke ragẽwo daga gare su, kuma wurinMu akwai wani littãfi mai tsarẽwa.
- 5. Ã`a, sun ƙaryata ne game da gaskiyar a lõkacin da ta je musu, sabõda haka sunã a cikin wani al`amari mai raurawa.
- 6. Shin, to, ba su yi dubi ba zuwa ga samã a bisa gare su, yadda Muka gĩna ta, kuma Muka ƙawãce ta, kuma bã ta da waɗansu tsãgogi?
- 7. Da ƙasã, Mun mĩƙe ta, kuma Mun jẽfa kafaffun duwãtsu a cikinta, kuma Mun tsirar, a cikinta daga kõwane ma`auri mai ban sha`awa?
- 8. Dõmin wãyar da ido da tunãtarwa ga dukan bãwa mai tawakkali?
- 9. Kuma Mun sassakar, daga samã ruwa mai albarka sa`an nan Muka tsirar game da shi (itãcen) lambuna da ƙwãya abin girbẽwa.
- 10. Da itãcen dabĩno dõgãye, sunã da`ya`yan itãce gunda mãsu hauhawar jũna.
- 11. Dõmin arziki ga bãyi, kuma Muka rãyar da ƙasa matacciya game da shi. Kamar wannan ne fitar daga kabari kake.
- 12. Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu (mutãnen yanzu) da ma`abũta Rassi, da Samũdãwa.
- 13. Da Ãdãwa da Fir`auna da `yan`uwan Lũɗu.
- 14. Da ma`abũta ƙunci da mutãnen Tubba`u, kõwanensu ya ƙaryata Manzanni, sai ƙyacẽwaTa ta tabbata.
- 15. Shin, to, Mun kãsa ne game da halittar farko? Ã`a, su sunã a cikin rikici daga halitta sãbuwa.
- 16. Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun halitta mutum kuma Mun san abin da ransa ke yin waswãsi da shi, kuma Mũ ne mafi kusanta zuwa gare shi daga lakar jannayẽnsa.
- 17. A lõkacin da mãsu haɗuwa biyu suke haɗuwa daga dãma, kuma daga hagu akwai wani (malã`ika) zaunanne.
- 18. Bã ya lafazi da wata magana fãce a lĩƙe da shi akwai mai tsaro halartacce.
- 19. Kuma mãyen mutuwa ya jẽ da gaskiya. Wannan shĩ ne abin da ka kasance daga gare shi kanã bijirẽwa.
- 20. Kuma aka hũra a cikin ƙaho. Wancan yinin ƙyacẽwar ne fa.
- 21. Kuma kõwane rai ya zo, tãre da shi akwai mai kõra da mai shaida.
- 22. (Sai a ce masa): "Lalle ne, haƙĩƙa, ka kasance a cikin gafala daga wannan. To, Mun kuranye maka rufinka, sabõda haka ganinka a yau, mai kaifi ne."
- 23. Kuma abõkin haɗinsa ya ce: "Wannan shi ne abin da ke tãre da ni halarce."
- 24. (A ce wa Malã`iku), "Ku jẽfa, a cikin Jahannama, dukan mai yawan kãfirci, mai tsaurin rai."
- 25. "Mai yawan hanãwa ga alhẽri, mai zãlunci, mai shakka."
- 26. "Wanda ya sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, sabõda haka kujẽfa shi a cikin azãba mai tsanani."
- 27. Abõkin haɗinsa ya ce: "Ya Ubangijinmu! Ban sanya shi girman kai ba, kuma amma ya kasance a cikin ɓata mai nĩsa."
- 28. Ya ce: "Kada ku yi husũma a wuriNa, alhãli Na gabãtar da ƙyacewa zuwa gare ku."
- 29. "Ba a musanya magana a wuriNa, Kuma Ban zama Mai zãlunci ba ga bãyiNa."
- 30. Rãnar da Muke cẽwa ga Jahannama "Shin, kin cika?" Kuma ta ce: "Ashe, akwai wani ƙãri?"
- 31. Kuma a kusantar dã Aljanna ga mãsu taƙawa, ba da nĩsa ba.
- 32. "Wannan shĩ ne abin da ake yi muku wa`adi da shi ga dukan mai yawan kõmawa ga Allah, mai tsarewar (umurninSa).
- 33. "Wanda ya ji tsõron Mai rahama a fake, kuma ya zo da wata irin zũciya mai tawakkali."
- 34. (A ce musu) "Ku shige ta da aminci, waccan ita ce rãnar dawwama."
- 35. Sunã da abin da suke so a cikinta, kuma tãre da Mũ akwai ƙãrin ni`ima,
- 36. Kuma da yawa Muka halakar, a gabãninsu, (mutãnen yanzu) ɗaga waɗansu al`ummomi, (waɗanda suke) sũ ne mafi ƙarfin damƙa daga gare su, sa`an nan suka yi bincike a cikin ƙasãshe: `Kõ akwai wurin tsĩra`? (Babu).
- 37. Lalle ne, a cikin wancan, akwai tunãtarwa ga wanda zũciyarsa ta kasance gare shi, kõ kuwa ya jẽfa saurãro, alhãli kuwa yanã halarce (da hankalinsa).
- 38. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta sammai da ƙasã da abin da ke a tsakãninsu, a cikin kwãnaki shida, alhãli wata`yar wahala ba ta shãfe Mu ba.
- 39. Sabõda haka, ka yi haƙuri a kan abin da suke fadã, kuma ka yi tasĩhi game da gõdẽ wa Ubangijinka (watau ka yi salla) a gabãnin fitõwar rãnã da gabãnin ɓacẽwarta.
- 40. Kuma daga dare, sai ka yi tasbĩhi a gare Shi da bãyan sujada.
- 41. Kuma ka saurãra a rãnar da mai kira ke yin kira daga wuri makusanci.
- 42. Rãnar da suke saurãron tsãwa da gaskiya. Wancan shĩ ne yinin fita (daga kabari).
- 43. Lalle Mũ ne haƙĩƙa, Mu ne ke rãyarwa, kuma Mũ ne ke kashẽwa, kuma zuwa gare Mu kawai ne makõmar take.
- 44. Rãnar da ƙasã ke tsattsãgẽwa daga gare su, sunã mãsu gaggãwa. Wancan tãrãwar mutãne ne, mai sauƙi a gare Mu.
- 45. Mũ ne mafi sani game da abin da suke faɗi, kuma bã zã ka zama mai tĩlasta su ba. Sabõda haka ka tunatar game da Alƙur`ani, ga wanda ke tsõron ƙyacewaTa.
