logo HARUN YAHYA

An-Naba - ALQUR'ANI - Harun Yahya

  • 1. A kan mẽ suke tambayar jũna?
  • 2. A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur`ãni)?
  • 3. Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?
  • 4. A`aha! Zã su sani.
  • 5. Kuma, a`aha! Zã su sani.
  • 6. Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?
  • 7. Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?
  • 8. Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?
  • 9. Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?
  • 10. Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?
  • 11. Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?
  • 12. Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?
  • 13. Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?
  • 14. Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?
  • 15. Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?
  • 16. Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?
  • 17. Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.
  • 18. Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama`a jama`a.
  • 19. Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.
  • 20. Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.
  • 21. Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.
  • 22. Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.
  • 23. Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.
  • 24. Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.
  • 25. Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.
  • 26. Sakamako mai dãcẽwa.
  • 27. Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.
  • 28. Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyinMu, ƙaryatãwa!
  • 29. Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.
  • 30. Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.
  • 31. Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.
  • 32. Lambuna da inabõbi.
  • 33. Da cikakkun `yammata, tsãrar jũna.
  • 34. Da hinjãlan giya cikakku.
  • 35. Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.
  • 36. Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.
  • 37. Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.
  • 38. Rãnar da Rũhi da malã`iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.
  • 39. Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.
  • 40. Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"
SHARE
Facebook
X
WhatsApp
Telegram
QR Code
QR Code