logo HARUN YAHYA

Ad-Dukhan - ALQUR'ANI - Harun Yahya

  • 1. Ḥ. M̃.
  • 2. Inã rantsuwa da Littãfi Mabayyani.
  • 3. Lalle ne, Mũ, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mũ` Mun kasance Mãsu yin gargaɗi.
  • 4. A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kõwane umurui bayyananne.
  • 5. Umurni na daga wurinMu. Lalle Mũ ne Muka kasanceMãsu aikãwã.
  • 6. Sabõda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shĩ, Shi ne Mai ji, Mãsani.
  • 7. (Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).
  • 8. Babu abin bautãwa fãce Shi. Yana rãyarwa Kuma Yana kashẽwa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko.
  • 9. A`a sũ, sunã wãsã a cikin shakka.
  • 10. Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã tã zo da hayãƙi bayyananne.
  • 11. Yanã rufe mutãne. Wannan wata azãba ce mai raɗaɗi.
  • 12. Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne.
  • 13. Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?
  • 14. Sa`an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa ne, mahaukaci."
  • 15. Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).
  • 16. Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.
  • 17. Kuma lalle ne haƙĩƙa a gabaninsu, Mun fitini mutãnen Fir`auna, kuma wani Manzo karĩmi ya jẽ musu.
  • 18. (Mazon ya ce): "Ku kãwo mini (ĩmãninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku."
  • 19. "Kuma kada ku nẽmi ɗaukaka a kan Allah. Lalle nĩ mai zo muku ne da dalĩli bayyananne."
  • 20. "Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."
  • 21. "Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."
  • 22. Sai ya kirayi Ubangjinsa cẽwa waɗannan mutãnene mãsu laifi.
  • 23. (Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"
  • 24. "Kuma ka bar tẽku rarrabe. Lalle sũ, runduna ce abar nutsarwa."
  • 25. Da yawa suka bar gõnaki da marẽmari.
  • 26. Da shuke-shuke da matsayi mai kyau.
  • 27. Da wata ni`ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.
  • 28. Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.
  • 29. Sa`an nan samã da ƙasã ba su yi kũka a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.
  • 30. Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã`ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.
  • 31. Daga Fir`auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin mãsu ɓarna.
  • 32. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.
  • 33. Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu`ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni`ima bayyananna
  • 34. Lalle waɗannan mutãne, haƙĩka, sunã cẽwa,
  • 35. "Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."
  • 36. "Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance mãsu gaskiya."
  • 37. shin, sũ ne mafĩfĩta kõ kuwa mutãnen Tubba`u, kuma da waɗanda ke a gabãninsu? Mun halaka su, lalle sũ, sun kasance mãsu laifi.
  • 38. Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.
  • 39. Ba Mu halitta su ba fãce da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba.
  • 40. Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa`adinsu gabã ɗaya.
  • 41. Rãnar da wani zumu bã ya amfãnin wani zumu da kõme kuma ba su zama anã taimakon su ba.
  • 42. fãce wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
  • 43. Lalle itãciyar zaƙƙũm (ɗanyen wutã),
  • 44. Ita ce abincin mai laifi.
  • 45. Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.
  • 46. Kamar tafasar ruwan zãfi.
  • 47. (A cẽ wa malã`ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa`an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."
  • 48. "Sa`an nan ku zuba, a kansa, daga azãbar ruwan zãfi."
  • 49. (A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"
  • 50. "Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kunã shakka game da shi."
  • 51. Lalle mãsu taƙawa sunã cikin matsayi amintacce.
  • 52. A cikin gidãjen Aljanna da marẽmari.
  • 53. Sunã tufanta daga tufãfin alharĩni raƙĩƙi, da mai kauri, sunã mãsu zaman fuskantar jũna.
  • 54. Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mãtã mãsu kyaun idãnu, mãsu girmansu.
  • 55. Sunã kira, a cikinsu (gidẽjen) ga dukan `ya`yan itãcen marmari, sunã amintattu (daga dukan abin tsõro).
  • 56. Bã su ɗanɗanar mutuwa, a cikinsu, fãce mutuwar farko, kuma (Allah), Ya tsare musu azãbar Jahĩm.
  • 57. Sabõda falala daga Ubangijinka. Wancan shi ne babban rabo, mai girma.
  • 58. Dõmin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur`ãni) da harshenka, tsammãninsu, su riƙa tunãwa.
  • 59. Sai ka yi jira. Lalle sũ, mãsu jira ne.
SHARE
Facebook
X
WhatsApp
Telegram
QR Code
QR Code