68. Al-Qalam - Alqur'ani
- 1. Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
- 2. Kai, sabõda ni`imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
- 3. Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
- 4. Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
- 5. Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
- 6. Ga wanenku haukã take.
- 7. Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
- 8. Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
- 9. Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
- 10. Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
- 11. Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
- 12. Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
- 13. Mai girman kai, bãyan haka kuma la`ĩmi (bã ya son alhẽri).
- 14. Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
- 15. Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
- 16. Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
- 17. Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
- 18. Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
- 19. Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
- 20. Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
- 21. Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
- 22. Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
- 23. Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
- 24. "Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
- 25. Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
- 26. Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
- 27. "Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
- 28. Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
- 29. Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
- 30. Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
- 31. Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
- 32. "Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
- 33. Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
- 34. Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni`ima.
- 35. Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa`a kamar mãsu laifi?
- 36. Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
- 37. Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
- 38. Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
- 39. Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
- 40. Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
- 41. Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra`ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
- 42. Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.
- 43. Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
- 44. Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur`ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
- 45. Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.
- 46. Kõ kana tambayar su wata la`ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
- 47. Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
- 48. Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma`abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
- 49. Ba dõmin ni`ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
- 50. Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa`an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
- 51. Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur`ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
- 52. Shi (Alƙur`ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.
