Adh-Dhariyat - ALQUR'ANI - Harun Yahya
-
1. Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.
-
2. Sa`an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).
-
3. Sa`an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.
-
4. Sa`an nan da Malã`iku mãsu rabon al`amari (bisa umurnin Allah).
-
5. Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.
-
6. Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne
-
7. Inã rantsuwa da samã ma`abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).
-
8. Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur`ani).
-
9. Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).
-
10. An la`ani mãsu ƙiri-faɗi.
-
11. Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.
-
12. Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"
-
13. Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.
-
14. (A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."
-
15. Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.
-
16. Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).
-
17. Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.
-
18. Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.
-
19. Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.
-
20. Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.
-
21. Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?
-
22. Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.
-
23. To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,
-
24. Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?
-
25. A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"
-
26. Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa`an nan ya zo da maraƙi tutturna,
-
27. Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"
-
28. Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.
-
29. Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"
-
30. Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."
-
31. (Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al`almarinku, yã kũ Manzanni!"
-
32. Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.
-
33. "Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).
-
34. "Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."
-
35. Sa`an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.
-
36. Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.
-
37. Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.
-
38. Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir`auna da wani dalĩli bayyananne.
-
39. Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"
-
40. Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa`an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
-
41. Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.
-
42. Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.
-
43. Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"
-
44. Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.
-
45. Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.
-
46. Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.
-
47. Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.
-
48. Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,
-
49. Kuma daga kõme Mun halitta nau`i biyu, watakila zã ku yi tunãni.
-
50. Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
-
51. Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
-
52. Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."
-
53. shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã`a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.
-
54. Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.
-
55. Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.
-
56. Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.
-
57. Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.
-
58. Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.
-
59. To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
-
60. Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.
SHARE
1
Al-Fatihah
2
Al Baqara
3
Ali `Imran
4
An-Nisa
5
Al-Ma`idah
6
Al-An`am
7
Al-A`raf
8
Al-Anfal
9
At-Tawbah
10
Yunus
11
Hud
12
Yusuf
13
Ar-Ra`d
14
Ibrahim
15
Al-Hijr
16
An-Nahl
17
Al-Isra
18
Al-Kahf
19
Maryam
20
Taha
21
Al-Anbya
22
Al-Haj
23
Al-Mu`minun
24
An-Nur
25
Al-Furqan
26
Ash-Shu`ara
27
An-Naml
28
Al-Qasas
29
Al-`Ankabut
30
Ar-Rum
31
Luqman
32
As-Sajdah
33
Al-Ahzab
34
Saba
35
Faatir
36
Ya-Sin
37
As-Saffat
38
Sad
39
Az-Zumar
40
Ghafir
41
Fussilat
42
sh-Shuraa
43
Az-Zukhruf
44
Ad-Dukhan
45
Al-Jathiyah
46
Al-Ahqaf
47
Muhammad
48
Al-Fath
49
Al-Hujurat
50
Qaf
51
Adh-Dhariyat
52
At-Tur
53
An-Najm
54
Al-Qamar
55
Ar-Rahman
56
Al-Waqi`ah
57
Al-Hadid
58
Al-Mujadila
59
Al-Hashr
60
Al-Mumtahanah
61
As-Saf
62
Al-Jumu`ah
63
Al-Munafiqun
64
At-Taghabun
65
At-Talaq
66
At-Tahrim
67
Al-Mulk
68
Al-Qalam
69
Al-Haqqah
70
Al-Ma`arij
71
Nuh
72
Al-Jinn
73
Al-Muzzammil
74
Al-Muddaththir
75
Al-Qiyamah
76
Al-Insan
77
Al-Mursalat
78
An-Naba
79
An-Nazi`at
80
Abasa
81
At-Takwir
82
Al-Infitar
83
Al-Mutaffifin
84
Al-Inshiqaq
85
Al-Buruj
86
At-Tariq
87
Al-A`la
88
Al-Ghashiyah
89
Al-Fajr
90
Al-Balad
91
Ash-Shams
92
Al-Layl
93
Ad-Duhaa
94
Ash-Sharh
95
At-Tin
96
Al-`Alaq
97
Al-Qadr
98
Al-Bayyinah
99
Az-Zalzalah
100
Al-`Adiyat
101
Al-Qari`ah
102
At-Takathur
103
Al-`Asr
104
Al-Humazah
105
Al-Fil
106
Quraysh
107
Al-Ma`un
108
Al-Kawthar
109
Al-Kafirun
110
An-Nasr
111
Al-Masad
112
Al-Ikhlas
113
Al-Falaq
114
An-Nas