71. Nuh - Alqur'ani
- 1. Lalle ne Mun aiki Nũhu zuwa ga mutãnensa, cẽwa ka yi gargaɗi ga mutãnenka gabãnin wata azãba mai raɗaɗi ta zo musu.
- 2. Ya ce: "Ya mutãnena ni, a gare ku, mai gargaɗi ne, mai bayyanãwa."
- 3. "Cewa ku bauta wa Allah, ku ji tsõronSa, kuma ku bĩ ni."
- 4. "Allah zai gãfarta muku daga zunubanku kuma Ya jinkirta muku zuwa ga ajalin da aka ambata. Lalle ne ajalin Allah idan ya zo, ba za a jinkirta Shi ba, dã kun kasance masana (ga abin da nake faɗã dã, kun bar kãfirci)."
- 5. Nũhu) ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne, na kirãyi mutãnena, a cikin dare da yini."
- 6. "To, amma kirana bai ƙãre su ba sai da, gudu (daga gare ni)."
- 7. "Kuma lalle ne ni, kõ da yaushe na kirãye su dõmin Ka gãfarta musu, sai su sanya yatsunsu a cikin kunnuwansu, su lulluɓe da tufãfinsu, su dõge ga yin laifi. Sun yi girman kai iyãkar girman kai."
- 8. "Sa`an nan lalle ne ni, na kira su, a bayyane."
- 9. "Sa`an nan lalle ne, na yi yẽkuwa sabõda su, kuma na gãna da su a cikin asĩri."
- 10. "Shi na ce, `Ku nẽmi gãfara daga Ubangijinku, lalle ne shi Ya kasance Mai gãfara ne."
- 11. "Ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai ɓuɓɓuga."
- 12. "Kuma ya yalwata muku game da dũkiya da ɗiya, Ya sanya muku (albarka) ga gõnaki, kuma Ya sanya muku koguna."
- 13. "Me ya sãme ku, bã ku fãtar sãmun natsuwa daga Allah,"
- 14. "Alhãli kuwa, lalle ne, Ya halitta. ku, a cikin hãlãye?"
- 15. "Ba ku ga yadda Allah Ya halitta wasu sammai bakwai ɗabaƙõƙĩ a kan jũna ba?"
- 16. "Ya sanya watã a cikinsu, yana mai haske, Ya sanya rãnã babbar fitila?"
- 17. "Kuma Allah Ya tsirar da ku daga ƙasa (kamar ganye) tsirarwa."
- 18. "Sa`an nan Ya mayar da ku a cikinta, kuma Ya fitar da ku fitarwa."
- 19. "Kuma Allah Ya sanya muku ƙasa shimfidaɗɗiya."
- 20. "Dõmin ku shiga a cikinta, hanyõyi mãsu fãɗi."
- 21. Nũhu ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne sũ sun saɓa mini sun bi wanda dukiyarsa da ɗiyansa ba su ƙãre shi da kõme ba sai da hasãra."
- 22. "Kuma sun yi wani mãkirci, mãkirci babba."
- 23. "Kuma suka ce: Faufau kada ku bar gumãkanku, kuma faufau, kada ku bar wadda, kuma kada ku bar suwã kuma kada ku bar Yagũsa da Ya`ũƙa da Nasra."
- 24. "Kuma lalle ne sun ɓatar da (mutãne) mãsu yawa, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai (kõme) sai ɓata."
- 25. Sabõda laifukansu na ganganci aka nutsar da su, sa`an nan aka sanya su a wuta. Saboda haka ba su sãmã wa kansu wani mataimaki wanin Allah ba.
- 26. Kuma Nũhu ya ce: "Ya Ublngijina! Kada Ka bari, a kan ƙasa, daga cikin kãfirai, wanda ke zama a cikin gida."
- 27. "Lalle ne, Kai idan Ka bar su, zã su ɓatar da bãyinKa, kuma bã zã su haifi kowa ba fãce fãjiri mai yawan kãfirci"
- 28. "Ya Ubanginjina! Ka yi mini gãfara (ni) da mahaifana biyu, da wanda ya shiga gidana, yana mai ĩmãni, da mũminai maza da mũminai mãtã, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai kõme sai halaka."
