81. At-Takwir - Alqur'ani
- 1. Idan rãna aka shafe haskenta
- 2. Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
- 3. Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
- 4. Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
- 5. Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
- 6. Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
- 7. Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
- 8. Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
- 9. "Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
- 10. Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
- 11. Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
- 12. Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
- 13. Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
- 14. Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
- 15. To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
- 16. Mãsu gudu suna ɓũya.
- 17. Da dare idan ya bãyar da bãya.
- 18. Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
- 19. Lalle ne shi (Alƙur`ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
- 20. Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al`arshi.
- 21. Wanda ake yi wa ɗã`a (wato shugaban malã`iku) ne a can, amintacce.
- 22. Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
- 23. Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
- 24. Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
- 25. Kuma shi (Alƙur`ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la`ana, ba ce.
- 26. Shin, a inã zã ku tafi?
- 27. Lalle ne shi (Alƙur`ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
- 28. Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
- 29. Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.
