80. Abasa - Alqur'ani
- 1. Yã game huska kuma ya jũya bãya.
- 2. Sabõda makãho yã je masa.
- 3. To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
- 4. Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
- 5. Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
- 6. Sa`an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
- 7. To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
- 8. Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
- 9. Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
- 10. Kai kuma kã shagala ga barinsa!
- 11. A`aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
- 12. Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
- 13. (Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
- 14. Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
- 15. A cikin hannãyen mala`iku marubũta.
- 16. Mãsu daraja, mãsu ɗã`a ga Allah.
- 17. An la`ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
- 18. Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
- 19. Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa`an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
- 20. Sa`an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
- 21. Sa`an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
- 22. Sa`an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
- 23. Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
- 24. To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
- 25. Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
- 26. Sa`an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
- 27. Sa`an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
- 28. Da inabi da ciyãwa.
- 29. Da zaitũni da itãcen dabĩno.
- 30. Da lambuna, mãsu yawan itãce.
- 31. Da `yã`yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
- 32. Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
- 33. To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
- 34. Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan`uwansa.
- 35. Da uwarsa da ubansa.
- 36. Da mãtarsa da ɗiyansa.
- 37. Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha`ani da ya ishe shi.
- 38. Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
- 39. Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
- 40. Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
- 41. Baƙi zai rufe su.
- 42. Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).
