99. Az-Zalzalah - Alqur'ani
- 1. Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.
- 2. Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.
- 3. Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"
- 4. A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.
- 5. cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.
- 6. A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.
- 7. To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.
- 8. Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.
