37. As-Saffat - Alqur'ani
- 1. Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
- 2. Sa`an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
- 3. Sa`an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
- 4. Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
- 5. Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
- 6. Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
- 7. Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
- 8. Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama`a mafi ɗaukaka (Malã`iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
- 9. Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
- 10. Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
- 11. Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
- 12. Ã`a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
- 13. Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
- 14. Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
- 15. Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
- 16. "Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
- 17. "Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
- 18. Ka ce: "Na`am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
- 19. Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
- 20. Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
- 21. Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
- 22. Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
- 23. Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
- 24. Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
- 25. Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
- 26. Ã`a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
- 27. Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
- 28. Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
- 29. Suka ce: "Ã`a, ba ku kasance mũminai ba.
- 30. "Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã`a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
- 31. "Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
- 32. "Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
- 33. To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
- 34. Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
- 35. Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
- 36. Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
- 37. Ã`a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
- 38. Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
- 39. Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
- 40. Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
- 41. Waɗannan sunã da abinci sananne.
- 42. `Ya`yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
- 43. A cikin gidãjen Aljannar ni`ima.
- 44. A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
- 45. Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
- 46. Farã mai dãɗi ga mashãyan.
- 47. A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
- 48. Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
- 49. Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
- 50. Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
- 51. Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
- 52. Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
- 53. "Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
- 54. (Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
- 55. Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
- 56. Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
- 57. "Kuma bã dõmin ni`imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
- 58. "Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
- 59. "Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
- 60. Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
- 61. Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
- 62. Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
- 63. Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
- 64. Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
- 65. Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
- 66. To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa`an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
- 67. Sa`an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
- 68. Sa`an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
- 69. Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
- 70. Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
- 71. Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
- 72. Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
- 73. Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
- 74. Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
- 75. Kuma lalle, haƙĩƙa` Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
- 76. Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
- 77. Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
- 78. Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama`ar ƙarshe.
- 79. Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
- 80. Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
- 81. Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
- 82. Sã`an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
- 83. Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
- 84. A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
- 85. A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
- 86. "Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
- 87. "To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
- 88. Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
- 89. Sã`an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
- 90. Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
- 91. Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa`an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
- 92. "Me ya sãme ku, bã ku magana?"
- 93. Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
- 94. Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
- 95. Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
- 96. "Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
- 97. Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa`an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
- 98. Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
- 99. Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
- 100. "Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
- 101. Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
- 102. To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
- 103. To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
- 104. Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
- 105. "Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
- 106. Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
- 107. Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
- 108. Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
- 109. Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
- 110. Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
- 111. Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
- 112. Kuma Muka yi masa bushãra Da Is`hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
- 113. Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is`hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
- 114. Kuma lalle, Mun yi ni`ima ga Mũsã da Hãrũna.
- 115. Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
- 116. Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
- 117. Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
- 118. Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
- 119. Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
- 120. Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
- 121. Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
- 122. Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.
- 123. Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
- 124. A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
- 125. "Shin, kunã bauta wa Ba`al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
- 126. "Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
- 127. Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
- 128. Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
- 129. Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
- 130. Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
- 131. Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
- 132. Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
- 133. Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
- 134. A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
- 135. Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
- 136. Sã`an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
- 137. Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
- 138. Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
- 139. Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
- 140. A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
- 141. Sã`an nan ya yi ƙuri`a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
- 142. Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
- 143. To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
- 144. Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
- 145. Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
- 146. Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
- 147. Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
- 148. Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
- 149. Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da `ya`ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
- 150. Kõ kuma Mun halitta malã`iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
- 151. To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
- 152. "Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
- 153. Shin, Yã zãɓi `yã`ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
- 154. Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
- 155. Shin, bã ku tunãni?
- 156. Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
- 157. To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
- 158. Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
- 159. Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
- 160. Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
- 161. To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
- 162. Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
- 163. Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
- 164. "Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."
- 165. "Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
- 166. "Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
- 167. Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
- 168. "Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
- 169. "Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
- 170. Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
- 171. Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
- 172. Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
- 173. Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
- 174. Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
- 175. Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
- 176. Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
- 177. To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
- 178. Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
- 179. Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
- 180. Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
- 181. Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
- 182. Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.
