84. Al-Inshiqaq - Alqur'ani
- 1. Idan sama ta kẽce,
- 2. Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
- 3. Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
- 4. Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
- 5. Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
- 6. Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
- 7. To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
- 8. To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
- 9. Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
- 10. Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
- 11. To, zã shi dinga kiran halaka!
- 12. Kuma ya shiga sa`ĩr.
- 13. Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
- 14. Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
- 15. Na`am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
- 16. To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
- 17. Da dare, da abin da ya ƙunsa.
- 18. Da watã idan (haskensa) ya cika.
- 19. Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
- 20. To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
- 21. Kuma idan an karanta Alkur`ãni a kansu, bã su yin tawãli`u?
- 22. Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
- 23. Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
- 24. Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
- 25. Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.
