logo HARUN YAHYA

Al-Inshiqaq - ALQUR'ANI - Harun Yahya

  • 1. Idan sama ta kẽce,
  • 2. Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
  • 3. Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
  • 4. Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
  • 5. Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
  • 6. Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
  • 7. To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
  • 8. To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
  • 9. Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
  • 10. Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
  • 11. To, zã shi dinga kiran halaka!
  • 12. Kuma ya shiga sa`ĩr.
  • 13. Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
  • 14. Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
  • 15. Na`am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
  • 16. To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
  • 17. Da dare, da abin da ya ƙunsa.
  • 18. Da watã idan (haskensa) ya cika.
  • 19. Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
  • 20. To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
  • 21. Kuma idan an karanta Alkur`ãni a kansu, bã su yin tawãli`u?
  • 22. Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
  • 23. Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
  • 24. Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
  • 25. Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.
SHARE
Facebook
X
WhatsApp
Telegram
QR Code
QR Code