At-Tur - ALQUR'ANI - Harun Yahya
-
1. Inã rantsuwa da ¦ũr (Dũtsen Mũsã).
-
2. Da wani littãfi rubũtacce.
-
3. A cikin wata takardar fãta shimfiɗaɗɗa.
-
4. Da Gidan da aka rãyar da shi (da ibãda).
-
5. Da rufin nan da aka ɗaukaka.
-
6. Da tẽkun nan da aka cika (da ruwa).
-
7. Lalle, azãbar Ubangijinka, haƙĩƙa, mai aukuwa ce.
-
8. Bã ta da mai tunkuɗẽwa.
-
9. Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.
-
10. Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.
-
11. To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.
-
12. Waɗanda suke a cikin kududdufi sunã wãsã.
-
13. Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.
-
14. (A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."
-
15. "To, shin wannan sihiri ne kõ kuwa kũ ne bã ku gani?"
-
16. "Ku shigẽ ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai anã yi muku sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
-
17. Lalle, mãsu taƙawa, sunã a cikin gidãjen Aljanna da wata ni`ima.
-
18. Sunã mãsu jin dãɗi da abin da Ubangijinsu Ya ba su, kuma Ubangijinsu Ya tsãre musu azãbar Jahĩm.
-
19. (A ce musu): "Ku ci, ku sha, da ni`ima, dõmin abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
-
20. Sunã kishingiɗe a kan karagu waɗanda ke cikin sahu, kuma Muka aurar da su waɗansu mãtã mãsu farin idãnu, mãsu girmansu.
-
21. Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma zũriyarsu suka bĩ su ga ĩmãnin, Mun riskar da zũriyarsu da su, alhãli kuwa bã da Mun rage musu kõme ba daga aikinsu, kõwane mutum jingina ne ga abin da ya sana`anta.
-
22. Kuma Muka yalwata musu `ya`yan itãce da nãma irin wanda suke marmari.
-
23. Sunã mĩƙa wa jũnansu a cikinta hinjãlan giya, wadda bãbu yãsassar magana a cikinta, kuma bãbu jin nauyin zunubi.
-
24. Kuma waɗansu samãri nã gẽwayãwa a kansu, kamar dai sũ lu`ulu`u ne wanda ke kulle.
-
25. Waɗansunsu suka fuskanta zuwa ga waɗansu, sunã tambayar jũna.
-
26. Suka ce: "Lalle mũ mun kasance a gabãnin wannan (a dũniya) a cikin iyãlanmu munã jin tsõro."
-
27. "To, Allah Yã yi mana kyautar falala, kuma Yã tsare mana azãbar iskar zãfi."
-
28. "Lalle mũ mun kasance, a gãbanin haka, munã kiran sa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai kyautatãwa, Mai rahama."
-
29. To, ka tunãtar kai fa sabõda ni`imar Ubangjinka, bã bõka kake ba, kuma bã mahaukaci ba.
-
30. Shin zã su ce: "Mawãƙi ne, munã jiran, masĩfun mutuwa game da shĩ"?
-
31. Ka ce: "Ku yi jira, domin nĩ ma lalle inã a cikin mãsu jira tãre da ku."
-
32. Shin, hankulansu ne ke umarin su da wannan, kõ kuwa sũ wasu mutãne ne mãsu ƙetare haddi?
-
33. Shin, cẽwa suke yi: "Shi ne ke ƙãga faɗarsa"? Ã`a ba su dai yi ĩmãni ba.
-
34. Sai su zõ da wani lãbãri mai misãlinsa idan sun kasance sũmãsu gaskiya ne.
-
35. Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?
-
36. Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã`a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba.
-
37. Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?
-
38. Shin, sunã da wani tsãni ne wanda suke (hawa sunã) saurãron (lãbãrin samã) a cikinsa? Sai mai saurarõnsu ya zo da wani dalĩli bayyananne.
-
39. Shin, Yanã da `ya`ya mãtã ne kuma kũ, kunã da ɗiya maza ne?
-
40. Shin, kanã tambayar su wata ijãra ne, sabõda haka suka zama mãsu jin nauyin biyan tãrar?
-
41. Shin, a wurinsu akwai ilmin gaibi, sabõda haka sunã rubũtãwa?
-
42. Shin, sunã nufin wani kaidi ne? To, waɗanda suka kãfirta sũ ne waɗanda ake yi wa kaidi.
-
43. Shin, sunã da wani abin bautãwa ne wanda bã Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke yi na shirki!
-
44. Kuma idan sun ga wani ɓaɓɓake daga samã yãnã fãɗuwa, sai su ce wani girgije ne, mai hauhawar jũna.
-
45. To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sũmar da su a cikinsa.
-
46. Rãnar da kaidinsu bã ya wadãtar masu da kõme, kuma bã a taimakon su.
-
47. Kuma lalle, waɗannan da suka yi zãluncin, sunã da azãba (a nan dũniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba.
-
48. Sai ka yi hakuri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kanã idãnunMu, kuma ka tsarkake Ubangijinka da (tasbĩhi) game da gõde Masa a lõkacin da kake tãshi tsaye (dõmin salla kõ wani abu).
-
49. Kuma daga dare, sai ka tsarkake Shi (da tasbĩhin) dalõkacin jũyãwar taurãri.
SHARE
1
Al-Fatihah
2
Al Baqara
3
Ali `Imran
4
An-Nisa
5
Al-Ma`idah
6
Al-An`am
7
Al-A`raf
8
Al-Anfal
9
At-Tawbah
10
Yunus
11
Hud
12
Yusuf
13
Ar-Ra`d
14
Ibrahim
15
Al-Hijr
16
An-Nahl
17
Al-Isra
18
Al-Kahf
19
Maryam
20
Taha
21
Al-Anbya
22
Al-Haj
23
Al-Mu`minun
24
An-Nur
25
Al-Furqan
26
Ash-Shu`ara
27
An-Naml
28
Al-Qasas
29
Al-`Ankabut
30
Ar-Rum
31
Luqman
32
As-Sajdah
33
Al-Ahzab
34
Saba
35
Faatir
36
Ya-Sin
37
As-Saffat
38
Sad
39
Az-Zumar
40
Ghafir
41
Fussilat
42
sh-Shuraa
43
Az-Zukhruf
44
Ad-Dukhan
45
Al-Jathiyah
46
Al-Ahqaf
47
Muhammad
48
Al-Fath
49
Al-Hujurat
50
Qaf
51
Adh-Dhariyat
52
At-Tur
53
An-Najm
54
Al-Qamar
55
Ar-Rahman
56
Al-Waqi`ah
57
Al-Hadid
58
Al-Mujadila
59
Al-Hashr
60
Al-Mumtahanah
61
As-Saf
62
Al-Jumu`ah
63
Al-Munafiqun
64
At-Taghabun
65
At-Talaq
66
At-Tahrim
67
Al-Mulk
68
Al-Qalam
69
Al-Haqqah
70
Al-Ma`arij
71
Nuh
72
Al-Jinn
73
Al-Muzzammil
74
Al-Muddaththir
75
Al-Qiyamah
76
Al-Insan
77
Al-Mursalat
78
An-Naba
79
An-Nazi`at
80
Abasa
81
At-Takwir
82
Al-Infitar
83
Al-Mutaffifin
84
Al-Inshiqaq
85
Al-Buruj
86
At-Tariq
87
Al-A`la
88
Al-Ghashiyah
89
Al-Fajr
90
Al-Balad
91
Ash-Shams
92
Al-Layl
93
Ad-Duhaa
94
Ash-Sharh
95
At-Tin
96
Al-`Alaq
97
Al-Qadr
98
Al-Bayyinah
99
Az-Zalzalah
100
Al-`Adiyat
101
Al-Qari`ah
102
At-Takathur
103
Al-`Asr
104
Al-Humazah
105
Al-Fil
106
Quraysh
107
Al-Ma`un
108
Al-Kawthar
109
Al-Kafirun
110
An-Nasr
111
Al-Masad
112
Al-Ikhlas
113
Al-Falaq
114
An-Nas