Al-Qamar - ALQUR'ANI - Harun Yahya
-
1. Sã`a ta yi kusa, kuma wata ya tsãge.
-
2. Kuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"
-
3. Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al`amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.
-
4. Kuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.
-
5. Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.
-
6. Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.
-
7. ¡asƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗandasuka wãtse.
-
8. Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cẽwa, "Wannan yini ne mai wuya!"
-
9. Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, sai suka ƙaryata BawanMu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsãwace shi.
-
10. Sabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako."
-
11. Sai Muka bũɗe kõfõfin sama da ruwa mai zuba.
-
12. Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasã ta zama idãnun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umurni da aka riga aka ƙaddara shi.
-
13. Kuma Muka ɗauke Nũhu a kan (jirgi) na alluna da ƙũsõshi.
-
14. Tanã gudãna, a kan idãnunMu, dõmin sakamako ga wanda aka yi wa kãfircin.
-
15. Kuma lalle, Mun bar ta ta zama ãyã. To, Shin, akwai mai tunãni
-
16. To, yãyã azãbãTa take da gargaɗiNa?
-
17. Kuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur`ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
-
18. Ãdãwa sun ƙaryata, to, yãya azãbãTa take, da gargaɗiNa?
-
19. Lalle Mũ, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahĩsa mai dõgẽwa.
-
20. Tanã fizgar mutãne kamar dai sũ kututturan dabĩno tumɓukakku ne.
-
21. To, yãya azãbãTa take da gargaɗiNa?
-
22. Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun sauƙaƙe Alƙur`ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
-
23. Samũdãwa sun ƙaryata game da gargaɗin.
-
24. Sai suka ce: "Wani mutum daga cikinmu, shi kaɗai, wai mu bĩ shi! Lalle mũ a lõkacin, haƙĩƙa mun shiga wata ɓata da haukã.
-
25. "Shin, an jẽfa masa Manzancin ne, a tsakãninmu? Ã`a, shĩ dai gawurtaccen maƙaryaci ne mai girman kai!"
-
26. Zã su sani a gõbe, wãne ne gawurtaccen mai ƙaryar, mai girman kan?
-
27. Lalle Mũ, mãsu aikãwa da rãƙumar ne, ta zame musu fitina, sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi haƙuri.
-
28. Kuma ka bã su lãbãri cẽwa ruwa rababbe ne a tsakãninsu (da rãƙumar), kõwane sha, mai shi yanã halartar sa.
-
29. Sai suka kira abokinsu, sai ya karɓa, sa`an nan ya sõke ta,
-
30. To, yãya azãbaTa take da gargaɗiNa?
-
31. Lalle Mũ, Mun aika tsãwa guda a kansu, sai suka kasance kamar yãyin mai shinge.
-
32. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur`ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
-
33. Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata, game da gargaɗi.
-
34. Lalle Mun aika iskar tsakuwa a kansu, fãce mabiyan Lũɗu, Mun tsirar da su a lõkacin asuba.
-
35. Sabõda wata ni`ima ta daga gare Mu. Kamar haka Muke sãka wa wanda ya gõde.
-
36. Kuma lalle, haƙĩƙa, ya yi musu gargaɗin damƙarMu, sai suka yi musu game da gargaɗin.
-
37. Kuma lalle haƙĩƙa, su, sun nẽme shi ta wajen bãƙinsa, sai Muka shãfe idãnunsu. "To, ku ɗanɗani azãbaTa da gargaɗĩNa."
-
38. Kuma lalle, haƙĩƙa, wata azãba matabbaciya tã wãye musu gari da yãƙi, tun da sãfe.
-
39. To, ku ɗanɗani azãbãTa da gargaɗĩNa.
-
40. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
-
41. Kuma lalle, haƙĩƙa, gargaɗin ya jẽ wa mabiyan Fir`auna.
-
42. Sun ƙaryata game da ãyõyinMu, dukansu sai Muka kãma su, irin kãmun Mabuwãyi, Mai ĩkon yi.
-
43. Shin, kãfiranku ne mafi alhẽri daga waɗancan, ko kuwa kunã da wata barã`a a cikin littattafai?
-
44. Kõ zã su ce: "Mũ duka mãsu haɗa ƙarfi ne dõmin cin nasara?"
-
45. Zã a karya tãron, kuma su jũya bãya dõmin gudu.
-
46. Ã`a, Sã`a ita cẽ lõkacin wa`adinsu, kuma Sã`ar tã fi tsananin masĩfa, kuma ta fiɗãci.
-
47. Lalle ne, mãsu laifi sunã a cikin ɓata da hauka.
-
48. Rãnar da zã a jã su a cikin wuta a kan fuskõkinsu. "Ku ɗanɗani shãfar wutar Saƙar."
-
49. Lalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri.
-
50. Kuma umurninMu bai zamo ba fãce da kalma ɗaya, kamar walƙãwar ido.
-
51. Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunãni?
-
52. Kuma kõwane abu, da suka aikata shi, yanã a cikin littattafai.
-
53. Kuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne.
-
54. Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna da kõguna.
-
55. A cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa.
SHARE
1
Al-Fatihah
2
Al Baqara
3
Ali `Imran
4
An-Nisa
5
Al-Ma`idah
6
Al-An`am
7
Al-A`raf
8
Al-Anfal
9
At-Tawbah
10
Yunus
11
Hud
12
Yusuf
13
Ar-Ra`d
14
Ibrahim
15
Al-Hijr
16
An-Nahl
17
Al-Isra
18
Al-Kahf
19
Maryam
20
Taha
21
Al-Anbya
22
Al-Haj
23
Al-Mu`minun
24
An-Nur
25
Al-Furqan
26
Ash-Shu`ara
27
An-Naml
28
Al-Qasas
29
Al-`Ankabut
30
Ar-Rum
31
Luqman
32
As-Sajdah
33
Al-Ahzab
34
Saba
35
Faatir
36
Ya-Sin
37
As-Saffat
38
Sad
39
Az-Zumar
40
Ghafir
41
Fussilat
42
sh-Shuraa
43
Az-Zukhruf
44
Ad-Dukhan
45
Al-Jathiyah
46
Al-Ahqaf
47
Muhammad
48
Al-Fath
49
Al-Hujurat
50
Qaf
51
Adh-Dhariyat
52
At-Tur
53
An-Najm
54
Al-Qamar
55
Ar-Rahman
56
Al-Waqi`ah
57
Al-Hadid
58
Al-Mujadila
59
Al-Hashr
60
Al-Mumtahanah
61
As-Saf
62
Al-Jumu`ah
63
Al-Munafiqun
64
At-Taghabun
65
At-Talaq
66
At-Tahrim
67
Al-Mulk
68
Al-Qalam
69
Al-Haqqah
70
Al-Ma`arij
71
Nuh
72
Al-Jinn
73
Al-Muzzammil
74
Al-Muddaththir
75
Al-Qiyamah
76
Al-Insan
77
Al-Mursalat
78
An-Naba
79
An-Nazi`at
80
Abasa
81
At-Takwir
82
Al-Infitar
83
Al-Mutaffifin
84
Al-Inshiqaq
85
Al-Buruj
86
At-Tariq
87
Al-A`la
88
Al-Ghashiyah
89
Al-Fajr
90
Al-Balad
91
Ash-Shams
92
Al-Layl
93
Ad-Duhaa
94
Ash-Sharh
95
At-Tin
96
Al-`Alaq
97
Al-Qadr
98
Al-Bayyinah
99
Az-Zalzalah
100
Al-`Adiyat
101
Al-Qari`ah
102
At-Takathur
103
Al-`Asr
104
Al-Humazah
105
Al-Fil
106
Quraysh
107
Al-Ma`un
108
Al-Kawthar
109
Al-Kafirun
110
An-Nasr
111
Al-Masad
112
Al-Ikhlas
113
Al-Falaq
114
An-Nas