logo HARUN YAHYA

An-Nazi`at - ALQUR'ANI - Harun Yahya

  • 1. Ina rantsuwa da mala`iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
  • 2. Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
  • 3. Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
  • 4. Sa`an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
  • 5. Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
  • 6. Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
  • 7. Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
  • 8. Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
  • 9. Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
  • 10. Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
  • 11. "Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
  • 12. Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
  • 13. To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
  • 14. Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
  • 15. Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
  • 16. A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
  • 17. Ka tafi zuwa ga Fir`auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
  • 18. "Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
  • 19. "Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
  • 20. Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
  • 21. Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
  • 22. Sa`an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
  • 23. Sai ya yi gayya, sa`an nan ya yi kira.
  • 24. Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
  • 25. Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
  • 26. Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
  • 27. Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
  • 28. Ya ɗaukaka rufinta, sa`an nan Ya daidaita ta.
  • 29. Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
  • 30. Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
  • 31. Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
  • 32. Da duwatsu, Yã kafe ta.
  • 33. Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
  • 34. To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
  • 35. Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
  • 36. Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
  • 37. To, amma wanda ya yi girman kai.
  • 38. Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
  • 39. To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
  • 40. Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
  • 41. To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
  • 42. Sunã tambayar ka game da sa`a, wai yaushe ne matabbatarta?
  • 43. Me ya haɗã ka da ambatonta?
  • 44. Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al`amarinta yake.
  • 45. Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
  • 46. Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
SHARE
Facebook
X
WhatsApp
Telegram
QR Code
QR Code