79. An-Nazi`at - Alqur'ani
- 1. Ina rantsuwa da mala`iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
- 2. Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
- 3. Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
- 4. Sa`an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
- 5. Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
- 6. Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
- 7. Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
- 8. Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
- 9. Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
- 10. Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
- 11. "Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
- 12. Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
- 13. To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
- 14. Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
- 15. Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
- 16. A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
- 17. Ka tafi zuwa ga Fir`auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
- 18. "Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
- 19. "Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
- 20. Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
- 21. Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
- 22. Sa`an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
- 23. Sai ya yi gayya, sa`an nan ya yi kira.
- 24. Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
- 25. Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
- 26. Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
- 27. Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
- 28. Ya ɗaukaka rufinta, sa`an nan Ya daidaita ta.
- 29. Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
- 30. Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
- 31. Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
- 32. Da duwatsu, Yã kafe ta.
- 33. Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
- 34. To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
- 35. Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
- 36. Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
- 37. To, amma wanda ya yi girman kai.
- 38. Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
- 39. To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
- 40. Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
- 41. To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
- 42. Sunã tambayar ka game da sa`a, wai yaushe ne matabbatarta?
- 43. Me ya haɗã ka da ambatonta?
- 44. Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al`amarinta yake.
- 45. Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
- 46. Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
