69. Al-Haqqah - Alqur'ani
- 1. Kiran gaskiya!
- 2. Mẽne ne kiran gaskiya?
- 3. Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
- 4. Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
- 5. To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
- 6. Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
- 7. (Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.
- 8. To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?
- 9. Kuma Fir`auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
- 10. Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
- 11. Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
- 12. Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
- 13. To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
- 14. Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
- 15. A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
- 16. Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
- 17. Kuma malã`iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã`iku) takwas na ɗauke da Al`arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
- 18. A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
- 19. To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
- 20. "Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
- 21. Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
- 22. A cikin Aljanna maɗaukakiya.
- 23. Nunannun `yã`yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
- 24. (Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni`ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
- 25. Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
- 26. "Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
- 27. "In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
- 28. "Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
- 29. "Ĩkona ya ɓace mini!"
- 30. (Sai a ce wa malã`iku) "Ku kãmã shi, sa`an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
- 31. "Sa`an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
- 32. "Sa`an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã`i saba`in, sai ku sanya shi."
- 33. "Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
- 34. "Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"
- 35. "Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
- 36. "Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
- 37. "Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
- 38. To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
- 39. Da abin da bã ku iya gani.
- 40. Lalle ne, shi (Alƙur`ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
- 41. Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
- 42. Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
- 43. Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
- 44. Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
- 45. Dã Mun kãma shi da dãma.
- 46. sa`an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
- 47. Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.
- 48. Kuma lalle ne shi (Alƙur`ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
- 49. Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
- 50. Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
- 51. Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
- 52. Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.
