96. Al-`Alaq - Alqur'ani
- 1. Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.
- 2. Ya hahitta mutum daga gudan jini.
- 3. Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.
- 4. Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.
- 5. Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.
- 6. A`aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).
- 7. Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.
- 8. Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.
- 9. Shin, kã ga wanda ke hana.
- 10. Bãwã idan yã yi salla?
- 11. Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?
- 12. Ko ya yi umurni da taƙawa?
- 13. Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?
- 14. Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?
- 15. A`aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.
- 16. Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.
- 17. Sai ya kirayi ƙungiyarsa.
- 18. Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala`iku mãsu girma).
- 19. A`aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali`u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).
