Al-Hijr - ALQUR'ANI - Harun Yahya
-
1. A. L̃.R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
-
2. Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.
-
3. Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa`an nan da sannu zã su sani.
-
4. Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
-
5. Wata al`umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
-
6. Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur`ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
-
7. "Dõmin me bã zã ka zo mana da malã`ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"
-
8. Bã Mu sassaukar da malã`iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
-
9. Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur`ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
-
10. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.
-
11. Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
-
12. Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
-
13. Bã su yin ĩmãni da shi, kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.
-
14. Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
-
15. Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã`a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
-
16. Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
-
17. Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
-
18. Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
-
19. Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
-
20. Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
-
21. Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
-
22. Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa`an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa`an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
-
23. Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.
-
24. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
-
25. Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
-
26. Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
-
27. Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi.
-
28. Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã`iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
-
29. "To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
-
30. Sai malã`iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
-
31. Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.
-
32. Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"
-
33. Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."
-
34. Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
-
35. "Kuma lalle ne akwai la`ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."
-
36. Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
-
37. Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."
-
38. "Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne."
-
39. Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
-
40. "Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
-
41. Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."
-
42. "Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."
-
43. Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma`a1kawartarsu gabã ɗaya.
-
44. Tanã da ƙõfõfi bakwai, ga kõwace ƙõfa akwai wani juz`i daga gare su rababbe.
-
45. Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
-
46. "Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."
-
47. Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama `yan`uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
-
48. Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikinta ba.
-
49. Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.
-
50. Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi.
-
51. Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.
-
52. A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."
-
53. Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."
-
54. Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"
-
55. Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
-
56. Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?"
-
57. Ya ce: "To, mẽne ne babban al`amarinku? Yã kũ manzanni!"
-
58. Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."
-
59. "Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
-
60. "Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
-
61. To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,
-
62. Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
-
63. Suka ce: "Ã`a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."
-
64. "Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."
-
65. "Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."
-
66. Kuma Muka hukunta wancan al`amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.
-
67. Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
-
68. Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
-
69. "Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
-
70. Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"
-
71. Ya ce: "Ga waɗannan, `ya`yãna idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
-
72. Rantsuwa da rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
-
73. Sa`an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
-
74. Sa`an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
-
75. Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
-
76. Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.
-
77. Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.
-
78. Kuma lalle ne ma`abũta Al`aika sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
-
79. Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.
-
80. Kuma lalle ne haƙĩƙa ma`abũta Hijiri sun ƙaryata Manzanni.
-
81. Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.
-
82. Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
-
83. Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.
-
84. Sa`an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.
-
85. Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã`a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
-
86. Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.
-
87. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur`ãni mai girma.
-
88. Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau`i-nau`i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
-
89. Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne."
-
90. Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,
-
91. Waɗanda suka sanya Alƙur`ãni tãtsuniyõyi.
-
92. To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
-
93. Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
-
94. Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
-
95. Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu izgili.
-
96. Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa`an nan da sannu zã su sani.
-
97. Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
-
98. Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
-
99. Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.
SHARE
1
Al-Fatihah
2
Al Baqara
3
Ali `Imran
4
An-Nisa
5
Al-Ma`idah
6
Al-An`am
7
Al-A`raf
8
Al-Anfal
9
At-Tawbah
10
Yunus
11
Hud
12
Yusuf
13
Ar-Ra`d
14
Ibrahim
15
Al-Hijr
16
An-Nahl
17
Al-Isra
18
Al-Kahf
19
Maryam
20
Taha
21
Al-Anbya
22
Al-Haj
23
Al-Mu`minun
24
An-Nur
25
Al-Furqan
26
Ash-Shu`ara
27
An-Naml
28
Al-Qasas
29
Al-`Ankabut
30
Ar-Rum
31
Luqman
32
As-Sajdah
33
Al-Ahzab
34
Saba
35
Faatir
36
Ya-Sin
37
As-Saffat
38
Sad
39
Az-Zumar
40
Ghafir
41
Fussilat
42
sh-Shuraa
43
Az-Zukhruf
44
Ad-Dukhan
45
Al-Jathiyah
46
Al-Ahqaf
47
Muhammad
48
Al-Fath
49
Al-Hujurat
50
Qaf
51
Adh-Dhariyat
52
At-Tur
53
An-Najm
54
Al-Qamar
55
Ar-Rahman
56
Al-Waqi`ah
57
Al-Hadid
58
Al-Mujadila
59
Al-Hashr
60
Al-Mumtahanah
61
As-Saf
62
Al-Jumu`ah
63
Al-Munafiqun
64
At-Taghabun
65
At-Talaq
66
At-Tahrim
67
Al-Mulk
68
Al-Qalam
69
Al-Haqqah
70
Al-Ma`arij
71
Nuh
72
Al-Jinn
73
Al-Muzzammil
74
Al-Muddaththir
75
Al-Qiyamah
76
Al-Insan
77
Al-Mursalat
78
An-Naba
79
An-Nazi`at
80
Abasa
81
At-Takwir
82
Al-Infitar
83
Al-Mutaffifin
84
Al-Inshiqaq
85
Al-Buruj
86
At-Tariq
87
Al-A`la
88
Al-Ghashiyah
89
Al-Fajr
90
Al-Balad
91
Ash-Shams
92
Al-Layl
93
Ad-Duhaa
94
Ash-Sharh
95
At-Tin
96
Al-`Alaq
97
Al-Qadr
98
Al-Bayyinah
99
Az-Zalzalah
100
Al-`Adiyat
101
Al-Qari`ah
102
At-Takathur
103
Al-`Asr
104
Al-Humazah
105
Al-Fil
106
Quraysh
107
Al-Ma`un
108
Al-Kawthar
109
Al-Kafirun
110
An-Nasr
111
Al-Masad
112
Al-Ikhlas
113
Al-Falaq
114
An-Nas