77. Al-Mursalat - Alqur'ani
- 1. Ina rantsuwa da iskõkin da ake sakõwa jẽre, sunã bin jũna.
- 2. Sa`an nan, su zamã iskõki mãsu ƙarfi suna kaɗãwa da ƙarfi.
- 3. Kuma, mãsu watsa rahama wãtsãwa.
- 4. sa`an nan, da ãyõyi mãsu rarrabe gaskiya da ƙarya rarrabẽwa.
- 5. Sa`an nan da malã`iku mãsu jẽfa tunãtarwa ga Manzanni.
- 6. Domin yanke hamzari ko dõmin gargadi.
- 7. Lalle ne, abin da ake yi muku wa`adi da shi tabbas mai aukuwa ne
- 8. To, idan taurãri aka shãfe haskensu.
- 9. Kuma, idan sama aka tsãge ta.
