75. Al-Qiyamah - Alqur'ani
- 1. Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.
- 2. Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.
- 3. Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?
- 4. Na`am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.
- 5. Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
- 6. Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"
- 7. To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
- 8. Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
- 9. Aka tãra rãnã da watã
- 10. Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"
- 11. A`aha! bãbu mafaka.
- 12. zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
- 13. Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
- 14. Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.
- 15. Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
- 16. Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur`ãni).
- 17. Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
- 18. To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.
- 19. sa`an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
- 20. A`aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
- 21. Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
- 22. Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
- 23. Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.
- 24. Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
- 25. Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.
- 26. A`aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.
- 27. kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"
- 28. Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.
- 29. Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
- 30. Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.
- 31. To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!
- 32. Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
- 33. Sa`an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.
- 34. Halaka tã tabbata a gare ka, sa`an nan ita ce mafi dãcewa.
- 35. Sa`an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
- 36. Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
- 37. Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)
- 38. Sa`an nan, ya zama gudan jini, sa`an nan Allah Ya halitta shi, sa`an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
- 39. Sa`an nan, Ya sanya daga gare shi, nau`i biyu: namiji damace?
- 40. Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?
