Al-Qiyamah - ALQUR'ANI - Harun Yahya
-
1. Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.
-
2. Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.
-
3. Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?
-
4. Na`am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.
-
5. Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
-
6. Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"
-
7. To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
-
8. Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
-
9. Aka tãra rãnã da watã
-
10. Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"
-
11. A`aha! bãbu mafaka.
-
12. zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
-
13. Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
-
14. Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.
-
15. Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
-
16. Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur`ãni).
-
17. Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
-
18. To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.
-
19. sa`an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
-
20. A`aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
-
21. Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
-
22. Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
-
23. Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.
-
24. Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
-
25. Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.
-
26. A`aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.
-
27. kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"
-
28. Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.
-
29. Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
-
30. Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.
-
31. To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!
-
32. Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
-
33. Sa`an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.
-
34. Halaka tã tabbata a gare ka, sa`an nan ita ce mafi dãcewa.
-
35. Sa`an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
-
36. Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
-
37. Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)
-
38. Sa`an nan, ya zama gudan jini, sa`an nan Allah Ya halitta shi, sa`an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
-
39. Sa`an nan, Ya sanya daga gare shi, nau`i biyu: namiji damace?
-
40. Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?
SHARE
1
Al-Fatihah
2
Al Baqara
3
Ali `Imran
4
An-Nisa
5
Al-Ma`idah
6
Al-An`am
7
Al-A`raf
8
Al-Anfal
9
At-Tawbah
10
Yunus
11
Hud
12
Yusuf
13
Ar-Ra`d
14
Ibrahim
15
Al-Hijr
16
An-Nahl
17
Al-Isra
18
Al-Kahf
19
Maryam
20
Taha
21
Al-Anbya
22
Al-Haj
23
Al-Mu`minun
24
An-Nur
25
Al-Furqan
26
Ash-Shu`ara
27
An-Naml
28
Al-Qasas
29
Al-`Ankabut
30
Ar-Rum
31
Luqman
32
As-Sajdah
33
Al-Ahzab
34
Saba
35
Faatir
36
Ya-Sin
37
As-Saffat
38
Sad
39
Az-Zumar
40
Ghafir
41
Fussilat
42
sh-Shuraa
43
Az-Zukhruf
44
Ad-Dukhan
45
Al-Jathiyah
46
Al-Ahqaf
47
Muhammad
48
Al-Fath
49
Al-Hujurat
50
Qaf
51
Adh-Dhariyat
52
At-Tur
53
An-Najm
54
Al-Qamar
55
Ar-Rahman
56
Al-Waqi`ah
57
Al-Hadid
58
Al-Mujadila
59
Al-Hashr
60
Al-Mumtahanah
61
As-Saf
62
Al-Jumu`ah
63
Al-Munafiqun
64
At-Taghabun
65
At-Talaq
66
At-Tahrim
67
Al-Mulk
68
Al-Qalam
69
Al-Haqqah
70
Al-Ma`arij
71
Nuh
72
Al-Jinn
73
Al-Muzzammil
74
Al-Muddaththir
75
Al-Qiyamah
76
Al-Insan
77
Al-Mursalat
78
An-Naba
79
An-Nazi`at
80
Abasa
81
At-Takwir
82
Al-Infitar
83
Al-Mutaffifin
84
Al-Inshiqaq
85
Al-Buruj
86
At-Tariq
87
Al-A`la
88
Al-Ghashiyah
89
Al-Fajr
90
Al-Balad
91
Ash-Shams
92
Al-Layl
93
Ad-Duhaa
94
Ash-Sharh
95
At-Tin
96
Al-`Alaq
97
Al-Qadr
98
Al-Bayyinah
99
Az-Zalzalah
100
Al-`Adiyat
101
Al-Qari`ah
102
At-Takathur
103
Al-`Asr
104
Al-Humazah
105
Al-Fil
106
Quraysh
107
Al-Ma`un
108
Al-Kawthar
109
Al-Kafirun
110
An-Nasr
111
Al-Masad
112
Al-Ikhlas
113
Al-Falaq
114
An-Nas