70. Al-Ma`arij - Alqur'ani
- 1. Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
- 2. Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
- 3. Daga Allah Mai matãkala.
- 4. Malã`iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
- 5. Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
- 6. Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
- 7. Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
- 8. Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
- 9. Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
- 10. Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.
- 11. Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
- 12. Da matarsa da ɗan`uwansa.
- 13. Da danginsa, mãsu tattarã shi.
- 14. Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa`an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
- 15. A`aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
- 16. Mai twãle fãtar goshi.
- 17. Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
- 18. Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
- 19. Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
- 20. Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
- 21. Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
- 22. Sai mãsu yin salla,
- 23. Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
- 24. Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
- 25. Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
- 26. Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
- 27. Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
- 28. Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
- 29. Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
- 30. Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
- 31. To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
- 32. Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
- 33. Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
- 34. Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
- 35. Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
- 36. Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
- 37. Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama`a-jama`a!
- 38. Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni`ima ne (ba da wani aiki ba)?
- 39. A`aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
- 40. Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
- 41. Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.
- 42. Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).
- 43. Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.
- 44. Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)
