Al-Ma`arij - ALQUR'ANI - Harun Yahya
-
1. Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
-
2. Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
-
3. Daga Allah Mai matãkala.
-
4. Malã`iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
-
5. Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
-
6. Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
-
7. Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
-
8. Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
-
9. Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
-
10. Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.
-
11. Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
-
12. Da matarsa da ɗan`uwansa.
-
13. Da danginsa, mãsu tattarã shi.
-
14. Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa`an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
-
15. A`aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
-
16. Mai twãle fãtar goshi.
-
17. Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
-
18. Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
-
19. Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
-
20. Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
-
21. Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
-
22. Sai mãsu yin salla,
-
23. Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
-
24. Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
-
25. Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
-
26. Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
-
27. Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
-
28. Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
-
29. Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
-
30. Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
-
31. To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
-
32. Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
-
33. Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
-
34. Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
-
35. Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
-
36. Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
-
37. Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama`a-jama`a!
-
38. Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni`ima ne (ba da wani aiki ba)?
-
39. A`aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
-
40. Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
-
41. Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.
-
42. Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).
-
43. Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.
-
44. Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)
SHARE
1
Al-Fatihah
2
Al Baqara
3
Ali `Imran
4
An-Nisa
5
Al-Ma`idah
6
Al-An`am
7
Al-A`raf
8
Al-Anfal
9
At-Tawbah
10
Yunus
11
Hud
12
Yusuf
13
Ar-Ra`d
14
Ibrahim
15
Al-Hijr
16
An-Nahl
17
Al-Isra
18
Al-Kahf
19
Maryam
20
Taha
21
Al-Anbya
22
Al-Haj
23
Al-Mu`minun
24
An-Nur
25
Al-Furqan
26
Ash-Shu`ara
27
An-Naml
28
Al-Qasas
29
Al-`Ankabut
30
Ar-Rum
31
Luqman
32
As-Sajdah
33
Al-Ahzab
34
Saba
35
Faatir
36
Ya-Sin
37
As-Saffat
38
Sad
39
Az-Zumar
40
Ghafir
41
Fussilat
42
sh-Shuraa
43
Az-Zukhruf
44
Ad-Dukhan
45
Al-Jathiyah
46
Al-Ahqaf
47
Muhammad
48
Al-Fath
49
Al-Hujurat
50
Qaf
51
Adh-Dhariyat
52
At-Tur
53
An-Najm
54
Al-Qamar
55
Ar-Rahman
56
Al-Waqi`ah
57
Al-Hadid
58
Al-Mujadila
59
Al-Hashr
60
Al-Mumtahanah
61
As-Saf
62
Al-Jumu`ah
63
Al-Munafiqun
64
At-Taghabun
65
At-Talaq
66
At-Tahrim
67
Al-Mulk
68
Al-Qalam
69
Al-Haqqah
70
Al-Ma`arij
71
Nuh
72
Al-Jinn
73
Al-Muzzammil
74
Al-Muddaththir
75
Al-Qiyamah
76
Al-Insan
77
Al-Mursalat
78
An-Naba
79
An-Nazi`at
80
Abasa
81
At-Takwir
82
Al-Infitar
83
Al-Mutaffifin
84
Al-Inshiqaq
85
Al-Buruj
86
At-Tariq
87
Al-A`la
88
Al-Ghashiyah
89
Al-Fajr
90
Al-Balad
91
Ash-Shams
92
Al-Layl
93
Ad-Duhaa
94
Ash-Sharh
95
At-Tin
96
Al-`Alaq
97
Al-Qadr
98
Al-Bayyinah
99
Az-Zalzalah
100
Al-`Adiyat
101
Al-Qari`ah
102
At-Takathur
103
Al-`Asr
104
Al-Humazah
105
Al-Fil
106
Quraysh
107
Al-Ma`un
108
Al-Kawthar
109
Al-Kafirun
110
An-Nasr
111
Al-Masad
112
Al-Ikhlas
113
Al-Falaq
114
An-Nas